fidelitybank

Majalisa ta dakatar da zaman ta sakamakon mutuwar mamban ta

Date:

Majalisar dattijai a ranar Talata, ta dakatar da zamanta kan mutuwar dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Egor/Ikpoba-Okha a Edo, Jude Ise-Idehen.

Ise-Idehen, har zuwa rasuwarsa, dan majalisar wakilai ne a karkashin jam’iyyar PDP.

Majalisar dattijai da ta dawo daga hutun makonni biyu, ta dage zamanta zuwa ranar 20 ga watan Yuli, domin karrama marigayin wanda ya rasu a ranar 1 ga watan Yuli yana da shekaru 52 a duniya.

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sen. Ajayi Boroffice (APC-Ondo) ne ya gabatar da kudirin dage zaman, sannan shugaban marasa rinjaye, Sen. Philip Aduda (PDP-FCT) ya goyi bayansa.

Majalisar dattijai, ta kuma yi shiru na minti daya don makokin marigayin kafin ta dakatar da zaman majalisar.

Majalisar ta samu jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ovie Omo-Agege (APC – Delta Central).

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya Ĉ™i amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ĉ˜ungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ĈŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Ĉ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Ĉ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Ĉ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buĈ™aci gwamnonin Ĉ™asar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp