fidelitybank

Mai Twitter ya nada ‘yan Najeriya 3 da za su jagoranci raba kudin Bitcoin

Date:

Mamallakin shafin sada zumunta na Twitter, Jack Dorsey, ya nada wasu ‘yan Najeriya Uku, da za su jagoranci shugabancin asusun amincewar Bitcoin.

Jack Dorsey, daya daga cikin wadanda suka kirkiri shafin Twitter ya nada ‘yan Najeriya uku da daya dan Afirka ta Kudu da su zama hukumar kula da asusun sa na Bitcoin Trust (BTrust) da za a raba domin ci gaban Afirka da Indiya.

A farkon watan Fabrairu, Dorsey ya ba da sanarwar BTrust tare da haɗin gwiwar mawakin gambara na rap dan Amurka, Jay Z.

BTrust asusu ne da ke da babban asusun BTC 500 wanda darajarsa ta kai N10,014,265,775.40 ($24,426,230), idan aka kwatanta shi da farashin kasuwar ranar Litinin dala $48,815.35, kuma ‘yan Afirka hudu ne za su sarrafa su, ba tare da kulawa daga Dorsey ko Jay Z ba.

A ranar Laraba, 15 ga watan Disamba, Dorsey ta wata sanarwa ya bayyana sunayen hukumar ta BTrust, wadanda uku daga cikinsu ‘yan Najeriya ne; Abubakar Nur Khalil da Obi Nwosu da Ojoma Ochai, da kuma Afirka ta Kudu, Carla Kirk-Cohen.

Idan za a iya tunawa a karshen watan Nuwamba, Dorsey ya yi murabus a matsayin shugaban Kamfanin Twitter.

Mista Dorsey, wanda ya kafa Twitter a 2006 tare da Biz Stone, Evan Williams, da Noah Glass ya na aiki a matsayin shugaba na Twitter da kuma kamfanin biyan kuɗi Square.

A cikin wata sanarwa da a ka fitar, ya rubuta, “Lokaci ya yi da zan tafi”, lura da cewa kamfanin “a shirye ya ke ya ci gaba.”

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp