Mutumin da ya auri mata 59 ya kuma haifi ‘ya’ya da jikoki 300, Mista Simon Odo, wanda a ka fi sani da ‘Sarkin Shaidan’ ya mutu.
Marigayi Odo, wanda ya fito daga yankin Aji a karamar hukumar Igbo-Eze ta Arewa a jihar Enugu, ya mutu ne da sanyin safiyar Talata bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya.
Mista Emeka Odo daya daga cikin ‘ya’yan da ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN, rasuwar mahaifinsa a gidansu ya ce,”Mahaifi na ya rasu ya na da shekaru 74 a duniya”.
Odo ya ce,”Tuni aka fara shirin binne mahaifi na bisa ga umarnin mahaifinsa ga mata da ‘ya’yansa cewa kada a ajiye gawarsa a dakin ajiyar gawa idan a ka tabbatar da mutuwarsa, amma a binne shi da wuri”.
“Eh mahaifina wanda a ka fi sani da Sarkin Shaidan ya mutu; Ya rasu ne a safiyar ranar Talata saboda ya yi jinya tsawon makonni uku da suka gabata. Muna yin taron dangi, domin kammala shirye-shiryen binne shi tunda ya umarce mu da kada mu sanya gawarsa a dakin ajiyar gawa,” inji shi.