Gwamna Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya nada tsohon shugaban karamar hukumar Nassarawa kuma tsohon shugaban kungiyar kananan hukumomin Najeriya ALGON reshen jihar Kano, daga shekarar 2018 zuwa 2021, Lamin Sani Zawiya a matsayin mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin kananan hukumomi. da Al’amuran Mulki.
Cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na gwamnan Kano, Abba Anwar ya sanyawa hannu a ka kuma rabawa manema labarai.
Ya ce nadin ya fara aiki ne tun daga ranar 2 ga watan Nuwamba, 2021, kamar yadda takardar ta nuna.
Dr Abdullahi Umar Ganduje ya kuma hori sabon mai bashi shawara a kan kananan hukumomi, Lamin Sani Zawaiya cewa da ya tsaya ya yi aikin sa bisa gaskiya darikon amana.