Dan wasan Manchester City Riyad Mahrez na shirin zama kyaftin din Algeria a gasar cin kofin nahiyar Afirka, saboda an sanya shi cikin jerin tawagar masu rike da kofin gasar.
Dan wasan mai shekaru 30 ya jagoranci Desert Fennecs ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka karo na biyu a Masar a shekarar 2019 bayan da ta doke Senegal da ci 1-0 a wasan karshe.
A ranar 11 ga watan Janairu ne Algeria za ta fara kare kambunta da Saliyo kafin ta kara da Equatorial Guinea da Ivory Coast a rukunin E.
Dan wasan gaba na Qatar, Baghdad Bounedjah, wanda ya ci waccan kwallon a shekarar 2019, yana daya daga cikin ‘yan wasa 12 da suka taimaka wa Algeria ta lashe kofin kasashen Larabawa na baya-bayan nan, kuma ya na cikin tawagar ‘yan wasa 28 da koci Djamel Belmadi zai buga a kasar Kamaru.