Hukumar tsaro ta Civil Defence, reshen jihar Osun, ta ce ta kama wasu mutane biyu, ciki akwai mahaifi da kaka, bisa zargin yi wa diyarsu mai shekaru 13 fyade.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Adigun Daniel, wanda ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Osogbo ranar Litinin.
Ya ce”an kama wadanda ake zargin ne a ranar Juma’a, bisa korafin da yarinyar ta yi, bayan mun yi bincike, yarinyar ta ce mahaifinta ya san ta tun shekaru biyu da suka wuce. Ta kuma ce ta na zaune da kakarta ta wajen uwa tun ta na da shekara uku kafin a kai ta wurin kakanta na wurin Uba ta na shekara biyar. Ta kuma ce mahaifinta da mahaifiyarta sun rabu, shi ya sa take zaune wajen kakanninta a lokuta daban-daban”.
Ya kara da cewar “Yarinyar ta kuma bayyana cewa, a wani lokaci, kakanta ya yi mata fyade, amma ta kasa tsayawa kan zarginta, saboda har yanzu tana zaune da shi,” A cewar Adigun.
Ya kuma tabbatar da cewa hukumar sun baiwa ma’aikatar harkokin mata da kananan yara ta jihar, domin ci gaba da kulawar yarinyar, har sai an kammala bincike kan lamarin.