Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya bayyana cewa wani matashi Yusuf ya rasa ransa a kamfanin Mamuda Group da ke Challawa, Jihar Kano, bayan da aka ce wani supervisor ya daɓa masa wuka.
Wasu rahotonnin dai daga Social Media sun ce an sallami matashin a aiki shi ne ya je karbar kudin sallama a nan supervisor din ya caka masa wuka.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da dangin mamacin ke kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike, tare da neman a tabbatar da adalci.
To amma a hirar da mahaifiyar marigayin ta yi da tashar Freedom Radio da ke Kano ta ce wanda ya caka masa wukar dama can suna da sabani tsawon lokaci.
Me kamfanin Mamuda Group ke cewa a kai?
Jamiʼin yada labaran kamfanin Bashir Alhasan Indabawa ya karyata wannan zargin cewa a kamfanin aka kashe matashi.
Ya ce, hatsaniyar ta faru ne tsakanin wasu ma’aikata biyu a wajen harabar kamfanin, kuma wanda ya caka wukar ba supervisor ba ne, dukkansu kananan maʼaikata ne a kamfanin.
Ya ƙara da cewa, suna da shaida cewa maʼaikatan su 2 sun bada uzri don fita daga kamfanin a wannan lokacin, kuma suna da bidiyo da kamfanin ya nada na duk abin da ya faru a harabarsa.
Ya ce, kuma duk da hakan ma’aikatan kamfanin ne suka kai wanda aka jikkata asibiti tare da hadin gwiwar ’yan sanda, kafin daga bisani ya rasu.
Yanzu haka dai ana ci gaba da jiran karin bayani daga rundunar ’yan sanda da sauran hukumomi, yayin da al’umma ke ci gaba da bayyana ra’ayoyi kan lamarin.