fidelitybank

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Date:

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya bayyana cewa wani matashi Yusuf ya rasa ransa a kamfanin Mamuda Group da ke Challawa, Jihar Kano, bayan da aka ce wani supervisor ya daɓa masa wuka.

Wasu rahotonnin dai daga Social Media sun ce an sallami matashin a aiki shi ne ya je karbar kudin sallama a nan supervisor din ya caka masa wuka.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da dangin mamacin ke kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike, tare da neman a tabbatar da adalci.

To amma a hirar da mahaifiyar marigayin ta yi da tashar Freedom Radio da ke Kano ta ce wanda ya caka masa wukar dama can suna da sabani tsawon lokaci.

Me kamfanin Mamuda Group ke cewa a kai?

Jamiʼin yada labaran kamfanin Bashir Alhasan Indabawa ya karyata wannan zargin cewa a kamfanin aka kashe matashi.

Ya ce, hatsaniyar ta faru ne tsakanin wasu ma’aikata biyu a wajen harabar kamfanin, kuma wanda ya caka wukar ba supervisor ba ne, dukkansu kananan maʼaikata ne a kamfanin.

Ya ƙara da cewa, suna da shaida cewa maʼaikatan su 2 sun bada uzri don fita daga kamfanin a wannan lokacin, kuma suna da bidiyo da kamfanin ya nada na duk abin da ya faru a harabarsa.

Ya ce, kuma duk da hakan ma’aikatan kamfanin ne suka kai wanda aka jikkata asibiti tare da hadin gwiwar ’yan sanda, kafin daga bisani ya rasu.

Yanzu haka dai ana ci gaba da jiran karin bayani daga rundunar ’yan sanda da sauran hukumomi, yayin da al’umma ke ci gaba da bayyana ra’ayoyi kan lamarin.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...
X whatsapp