fidelitybank

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Date:

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya bayyana cewa wani matashi Yusuf ya rasa ransa a kamfanin Mamuda Group da ke Challawa, Jihar Kano, bayan da aka ce wani supervisor ya daɓa masa wuka.

Wasu rahotonnin dai daga Social Media sun ce an sallami matashin a aiki shi ne ya je karbar kudin sallama a nan supervisor din ya caka masa wuka.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da dangin mamacin ke kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike, tare da neman a tabbatar da adalci.

To amma a hirar da mahaifiyar marigayin ta yi da tashar Freedom Radio da ke Kano ta ce wanda ya caka masa wukar dama can suna da sabani tsawon lokaci.

Me kamfanin Mamuda Group ke cewa a kai?

Jamiʼin yada labaran kamfanin Bashir Alhasan Indabawa ya karyata wannan zargin cewa a kamfanin aka kashe matashi.

Ya ce, hatsaniyar ta faru ne tsakanin wasu ma’aikata biyu a wajen harabar kamfanin, kuma wanda ya caka wukar ba supervisor ba ne, dukkansu kananan maʼaikata ne a kamfanin.

Ya ƙara da cewa, suna da shaida cewa maʼaikatan su 2 sun bada uzri don fita daga kamfanin a wannan lokacin, kuma suna da bidiyo da kamfanin ya nada na duk abin da ya faru a harabarsa.

Ya ce, kuma duk da hakan ma’aikatan kamfanin ne suka kai wanda aka jikkata asibiti tare da hadin gwiwar ’yan sanda, kafin daga bisani ya rasu.

Yanzu haka dai ana ci gaba da jiran karin bayani daga rundunar ’yan sanda da sauran hukumomi, yayin da al’umma ke ci gaba da bayyana ra’ayoyi kan lamarin.

Go back

Your message has been sent

Warning
Warning
Warning
Warning

Warning.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp