fidelitybank

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Date:

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele Sowore da hukumomin ƙasar ke tsare da shi ya yi kiran sakinsa cikin gaggawa.

Lauyoyin sun yi zargin cewa ana tsare da Sowore ƙarƙashin kulawar babban sifeton ƴansandan ƙasar, cikin hali maras kyau na tasku da cin zarafinsa, lamarin da suka ce yana barazana ga kariyarsa.

A ranar Laraba ne dai aka bayar da rahoton tsare Sowore bayan da ya amsa gayyatar jami’an ƴansanda domin amsa wasu tambayoyi.

Ɗaya daga cikin lauyoyin nasa da ya zanta da BBC a shaida cewa an gayyacci Sowore ne kan zarge-zargen laufukan bata suna da yin ƙaryar takardun ƴansanda.

Ya ce ƴansanda sun nuna musu wasu takardu na ƙorafi da aka rubuta kan Soworen, yana mai zargin ƴansanda da rubuta ɗaya daga ciki ƙorafe-ƙorafen.

Kawo yanzu dai hukumomin ƴansandan ba su ce komai ba game da tsare Soworen ba, kuma ba su mayar da amsar buƙatar da BBC ta gabatar musu na magana kan batun ba.

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International ta yi Allah wadai da ci gaba da tsare

Cikin wata sanarwa da ta fitar ta kira ga gwamnatin Najeriya ta saki ɗan gwagwarmayar tare da watsi da zarge-zargen da taje yi masa ba tare da wani sharaɗi ba.

Ƙungiyar ta kuma zargin gwamnatin Najeriya da tauye haƙƙin ƴan ƙasar maimaikon sauraron ra’ayinsu.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp