Gwamnatin Birtaniya ta ce za ta ɗage haramcin shiga ƙasarta ga dukkanin ƙasashe 11 da ta hana daga ranar Laraba.
Ƙasashen sun ƙunshi Angola da Botswana da Eswatini da Lesotho da Malawi da Mozambique da Namibia da Najeriya da Afrika ta Kudu da Zambia da kuma Zimbabwe.
A ƙarshen watan Nuwamba ne Birtaniya ta sake ɗaukar matakin na hana ƙasashen shiga ƙasarta saboda tsoron nau’in korona na Omicron.
Sakataren lafiya na ƙasar Sajid Javid ya ce,”Cutar ta ba zu sosai, domin hana matakin ba ya da wani amfani, za a ɗauki matakai na yin gwaji ga baƙi da suka shiga ƙasar, kuma duk wanda ya fito daga ƙasashen sai ya biya kuɗin otal na kwanaki 10 da zai killace kansa”.