A wani yunkuri na bunkasa harkokin wasanni a jihar Kano, Gwamnan jihar,Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya raba cekin kudi na Naira miliyan 96 ga kungiyoyin kwallon kafa 47 na jihar da ke shiga gasar kwallon kafa ta kasa.
A cewarsa, kudaden za su taimaka wa kungiyoyin masu son shiga gasar ta kasa ta kakar 2021/2022.
Gwamnan wanda mataimakinsa Dr.Nasiru Yusuf Gawuna ya wakilta a yayin bikin da aka gudanar a ranar Talata a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnatin Kano.
Ya kuma bayyana cewa dukkanin kungiyoyi 10 da za su fafata a rukunin na 1, kowacce kungiya za ta samu Naira miliyan 3, kungiyoyi 29 daga rukuni na biyu. kowanne zai samu Naira miliyan 2 yayin da kungiyoyi 8 daga ajin rukuni na 3 kowanne zai samu Naira miliyan 1.
Sanarwar mai kunshe da sa hannun Hassan Musa Fagge, wanda shine sakataren yada labarai na mataimakin gwamnan jihar Kano, Dr Nasiru Yusuf Gawuna.
Wannan alkawari ne da gwamnatin jihar Kano ta yi kuma ta cikawa kungiyoyin, kamar yadda sanarwar ta tabbatar da hakan.