Kungiyar goyon bayan Tinubu a Kano, ta ziyarci gidan su marigayiya Hanifa ‘yar shekaru 5 da mai makarantar su ya kashe ta, domin yi wa iyayen ta ta’aziya.
Cikin tawagar sun hadar da jagoranta Hon Lamin Sani wanda shi ne mai baiwa gwamnan Kano shawara a kan kananan hukumomi.
Sauran sun hadar da Hon. Yahaya Adamu Garun Ali da Hon. Abubakar Ali Minister da Hon. Abdullahi Mua’zu Gwarzo da kuma Malam Abdurrazaq da dai sauran su.