fidelitybank

Kudin da Jonathan ya bari ba za su iya rike Najeriya na tsawon makwanni 3 – Amaechi

Date:

Ministan harkokin Sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce kudaden da tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya bari, kadan ne da ba za su iya dawwama a Najeriya ba har tsawon makonni Uku kacal.

Amaechi ya bayyana hakan ne a lokacin wani shiri mai suna ‘Hard Copy’, na gidan Talabijin din Channels

Maupe Ogun-Yusuf, shi ne wanda ya kasance a shirin kuma ya tambayi ministan ko an tattauna batun tsaro a taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako-mako, sai ya amsa da cewa ba a tabo batun a can ba.

Da a ka kara tambayar ko shugaban ya fahimci matsalar, ministan cikin raha ya ce, “ko dan jaridan bai gane ba”.

Daga nan sai ya ci gaba da mayar da martani kan wannan tambayar, inda ya danganta talauci a matsayin babban dalilin da ke yin fashi da kuma wasu kalubalen da ke tunkarar Najeriya.

“Lokacin da ku ke magana game da ‘yan fashi da duk waɗannan mutanen da su ke kashewa. Tambaya ce a kan talauci. Kuma wannan talauci bai fara a wannan mulkin ba. Kar ku manta an sayar da mai a kan dala 110, dala 114 da 115 kowace ganga. Lokacin da wannan gwamnati ta hau mulki, man fetur ya fadi zuwa dala 28, kuma tun daga lokacin bai haura dala 80 kan kowacce ganga ba.”

“A matsayina na tsohon shugaban kungiyar gwamnonin (Amaechi ya taba zama gwamnan Rivers sau biyu), jami’an tsaro sun shaida min a taron da tsohon shugaban kasa ya jagoranta ciki har da tsohon ministan kudi cewa a kowane lokaci gwamnati dole ne a bar kudi a baya idan Najeriya ta fada yakin da zai dauki tsawon watanni shida.

“A lokacin da mu ka zo, ba su bar kudin da za su iya kai mu tsawon makonni uku ba. Kuma ina magana a wancan lokacin a matsayina na shugaban kungiyar gwamnonin.” A cewar Rotimi.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp