fidelitybank

Kudin da Jonathan ya bari ba za su iya rike Najeriya na tsawon makwanni 3 – Amaechi

Date:

Ministan harkokin Sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce kudaden da tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya bari, kadan ne da ba za su iya dawwama a Najeriya ba har tsawon makonni Uku kacal.

Amaechi ya bayyana hakan ne a lokacin wani shiri mai suna ‘Hard Copy’, na gidan Talabijin din Channels

Maupe Ogun-Yusuf, shi ne wanda ya kasance a shirin kuma ya tambayi ministan ko an tattauna batun tsaro a taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako-mako, sai ya amsa da cewa ba a tabo batun a can ba.

Da a ka kara tambayar ko shugaban ya fahimci matsalar, ministan cikin raha ya ce, “ko dan jaridan bai gane ba”.

Daga nan sai ya ci gaba da mayar da martani kan wannan tambayar, inda ya danganta talauci a matsayin babban dalilin da ke yin fashi da kuma wasu kalubalen da ke tunkarar Najeriya.

“Lokacin da ku ke magana game da ‘yan fashi da duk waɗannan mutanen da su ke kashewa. Tambaya ce a kan talauci. Kuma wannan talauci bai fara a wannan mulkin ba. Kar ku manta an sayar da mai a kan dala 110, dala 114 da 115 kowace ganga. Lokacin da wannan gwamnati ta hau mulki, man fetur ya fadi zuwa dala 28, kuma tun daga lokacin bai haura dala 80 kan kowacce ganga ba.”

“A matsayina na tsohon shugaban kungiyar gwamnonin (Amaechi ya taba zama gwamnan Rivers sau biyu), jami’an tsaro sun shaida min a taron da tsohon shugaban kasa ya jagoranta ciki har da tsohon ministan kudi cewa a kowane lokaci gwamnati dole ne a bar kudi a baya idan Najeriya ta fada yakin da zai dauki tsawon watanni shida.

“A lokacin da mu ka zo, ba su bar kudin da za su iya kai mu tsawon makonni uku ba. Kuma ina magana a wancan lokacin a matsayina na shugaban kungiyar gwamnonin.” A cewar Rotimi.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp