Ministan harkokin Sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce kudaden da tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya bari, kadan ne da ba za su iya dawwama a Najeriya ba har tsawon makonni Uku kacal.
Amaechi ya bayyana hakan ne a lokacin wani shiri mai suna ‘Hard Copy’, na gidan Talabijin din Channels
Maupe Ogun-Yusuf, shi ne wanda ya kasance a shirin kuma ya tambayi ministan ko an tattauna batun tsaro a taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako-mako, sai ya amsa da cewa ba a tabo batun a can ba.
Da a ka kara tambayar ko shugaban ya fahimci matsalar, ministan cikin raha ya ce, “ko dan jaridan bai gane ba”.
Daga nan sai ya ci gaba da mayar da martani kan wannan tambayar, inda ya danganta talauci a matsayin babban dalilin da ke yin fashi da kuma wasu kalubalen da ke tunkarar Najeriya.
“Lokacin da ku ke magana game da ‘yan fashi da duk waɗannan mutanen da su ke kashewa. Tambaya ce a kan talauci. Kuma wannan talauci bai fara a wannan mulkin ba. Kar ku manta an sayar da mai a kan dala 110, dala 114 da 115 kowace ganga. Lokacin da wannan gwamnati ta hau mulki, man fetur ya fadi zuwa dala 28, kuma tun daga lokacin bai haura dala 80 kan kowacce ganga ba.”
“A matsayina na tsohon shugaban kungiyar gwamnonin (Amaechi ya taba zama gwamnan Rivers sau biyu), jami’an tsaro sun shaida min a taron da tsohon shugaban kasa ya jagoranta ciki har da tsohon ministan kudi cewa a kowane lokaci gwamnati dole ne a bar kudi a baya idan Najeriya ta fada yakin da zai dauki tsawon watanni shida.
“A lokacin da mu ka zo, ba su bar kudin da za su iya kai mu tsawon makonni uku ba. Kuma ina magana a wancan lokacin a matsayina na shugaban kungiyar gwamnonin.” A cewar Rotimi.