Jami’an tsaro sun sake kwato titunan babban birnin Kazakhstan a yau Juma’a, bayan kwashe tsawon kwanaki a na tashe-tashen hankula.
Tuni dai shugaban kasar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayevk da ke samun goyon bayan Rasha ya umarci dakarunsa da su yi harbin kan mai uwa da wabi, domin murkushe zanga-zangar da a ke yi a fadin kasar.
Kwana guda bayan da Rusha ta aike da jami’an tsaro, domin su taimaka wajen murkushe ‘yan tawayen, wanda ‘yan sandan su ka ta yi sintiri a kan titunan birnin na Almaty da su ka karbe ikon sa, duk da kawo wannan lokaci a na iya jin karar harbe-harbe.
Mutane da dama ne suka mutu tare da kona gine-ginen jama’a a fadin Kazakhstan wanda mummunan tashin hankali da tsohuwar jamhuriyar Soviet ta fuskanta cikin shekaru 30 da samun ‘yancin kai.
Rahsa ta ce sama da jiragen sama 70 ne ke jigilar sojojin Rasha zuwa cikin Kazakhstan, kuma a halin yanzu, wanda a ka sake kwace filin sauka da tashin jirgi a ranar Alhamis daga wajen masu zanga-zangar.
Rikicin dai ya janyo tsoma bakin soji da Rasha ta yi a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin kasashen Gabas da Yamma a daidai lokacin da Rasha da Amurka ke shirin tattaunawa a mako mai zuwa kan rikicin Ukraine.
Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya zargi ‘yan ta’adda da a ka horar da su daga kasashen waje da hannu wajen tashe tashen hankula, ba tare da bayar da shaida ba.