fidelitybank

Ku yi harbi kan mai uwa dawabi ga masu zanga-zanga – Shugaban  Kazakhstan

Date:

Jami’an tsaro sun sake kwato titunan babban birnin Kazakhstan a yau Juma’a, bayan kwashe tsawon kwanaki a na tashe-tashen hankula.

Tuni dai shugaban kasar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayevk da ke samun goyon bayan Rasha ya umarci dakarunsa da su yi harbin kan mai uwa da wabi, domin murkushe zanga-zangar da a ke yi a fadin kasar.

Kwana guda bayan da Rusha ta aike da jami’an tsaro, domin su taimaka wajen murkushe ‘yan tawayen, wanda ‘yan sandan su ka ta yi sintiri a kan titunan birnin na Almaty da su ka karbe ikon sa, duk da kawo wannan lokaci a na iya jin karar harbe-harbe.

Mutane da dama ne suka mutu tare da kona gine-ginen jama’a a fadin Kazakhstan wanda mummunan tashin hankali da tsohuwar jamhuriyar Soviet ta fuskanta cikin shekaru 30 da samun ‘yancin kai.

Rahsa ta ce sama da jiragen sama 70 ne ke jigilar sojojin Rasha zuwa cikin Kazakhstan, kuma a halin yanzu, wanda a ka sake kwace filin sauka da tashin jirgi a ranar Alhamis daga wajen masu zanga-zangar.

Rikicin dai ya janyo tsoma bakin soji da Rasha ta yi a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin kasashen Gabas da Yamma a daidai lokacin da Rasha da Amurka ke shirin tattaunawa a mako mai zuwa kan rikicin Ukraine.

Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya zargi ‘yan ta’adda da a ka horar da su daga kasashen waje da hannu wajen tashe tashen hankula, ba tare da bayar da shaida ba.

 

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...
X whatsapp