fidelitybank

Ku yi harbi kan mai uwa dawabi ga masu zanga-zanga – Shugaban  Kazakhstan

Date:

Jami’an tsaro sun sake kwato titunan babban birnin Kazakhstan a yau Juma’a, bayan kwashe tsawon kwanaki a na tashe-tashen hankula.

Tuni dai shugaban kasar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayevk da ke samun goyon bayan Rasha ya umarci dakarunsa da su yi harbin kan mai uwa da wabi, domin murkushe zanga-zangar da a ke yi a fadin kasar.

Kwana guda bayan da Rusha ta aike da jami’an tsaro, domin su taimaka wajen murkushe ‘yan tawayen, wanda ‘yan sandan su ka ta yi sintiri a kan titunan birnin na Almaty da su ka karbe ikon sa, duk da kawo wannan lokaci a na iya jin karar harbe-harbe.

Mutane da dama ne suka mutu tare da kona gine-ginen jama’a a fadin Kazakhstan wanda mummunan tashin hankali da tsohuwar jamhuriyar Soviet ta fuskanta cikin shekaru 30 da samun ‘yancin kai.

Rahsa ta ce sama da jiragen sama 70 ne ke jigilar sojojin Rasha zuwa cikin Kazakhstan, kuma a halin yanzu, wanda a ka sake kwace filin sauka da tashin jirgi a ranar Alhamis daga wajen masu zanga-zangar.

Rikicin dai ya janyo tsoma bakin soji da Rasha ta yi a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin kasashen Gabas da Yamma a daidai lokacin da Rasha da Amurka ke shirin tattaunawa a mako mai zuwa kan rikicin Ukraine.

Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya zargi ‘yan ta’adda da a ka horar da su daga kasashen waje da hannu wajen tashe tashen hankula, ba tare da bayar da shaida ba.

 

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp