fidelitybank

Kotun Amurka ta bayar da izini a binciki gidan Trump

Date:

Wani alkali a Florida da ke Amurka ya sa an bude wasu daga cikin takardun da suka ba jami’an hukumar binciken manyan laifuka ta Amurkar FBI damar binciken gidan tsohon shugaban kasar Donald Trump, da ke Mar-a-Largo.

Mai shari’ar ya bayar da umarnin ne bayan da wasu kafafen yada labarai suka kafe cewa abu ne da ya shafi bukatar al’umma sanin bayanan da suka sa binciken.

Kawo yanzu dai abin da aka sani da ke kunshe a wadannan takardu karin bayanai ne game da takardar izinin gudanar da binciken, wadanda suka kara fayyace ainahin laifukan da ma’aikatar sharia’a ta Amurkar ke binciken tsohon shugaban Donald Trump.

Laifukan da suka hada da rike wasu bayanai na tsaron kasa da yin tarnaki ko hana gudanar da bincike na tarayya, ta hanyar fitar da wasu bayanai na gwamnati ba ta hanyar da doka ta tanada ba.

Duka wadannan sun bayyana ne bayan da wasu tarin kafafen yada labarai suka bukaci kotun ta bayar da umarnin bude takardar izinin gudanar da binciken, takardar wadda ta fayyace shedar da gwamnati take da ita kafin ta samu izinin yin binciken.

Lauyan Mista Trump ya yi maraba da hukuncin alkalin Bruce Reinhardt, amma kuma ya ce tsohon shugaban ya yi amanna akwai bukatar a bari jama’a su ga ainahin takardar izinin binciken gaba dayanta ba wata da aka sakaya wasu bayanai ba.

Yanzu mai shari’a Bruce Reinhardt ya bai wa jami’ai wa’adin mako daya, wato har zuwa ranar Alhamis na su bayar da shawara kan wadanne abubuwa ne za a iya fitarwa ga jama’a da kuma wadanda bai kamata a bayyana ba a cikin takardun. In ji BBC.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp