Kotun shari’ar misulunci mai zamanta a Ungogo karkashin jagorancin mai shari’a, Mansur Ibrahim ta hori wata mata da daurin talala na tsawon shekara guda, sakamakon satar Akuya.
Matar mai suna, Sailuba Abubakar Dawanau an gurfanar da ita ne a gaban kotun, bisa zargin satar Akuya, kuma lokacin da a ka karanta mata tuhumar, Sailuba ta amsa laifin ta nan take ba tare da ta wahalar da shari’a ba.
Mai shari’a, Mansur Ibrahim ya bayyana cewar, matar ta je wani gini na hukuma ta rinka yin shara a kullum daga safiya har zuwa yamma na tsahon shekara daya.