Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Fatakwal ta soke zaben ‘yan takarar majalisar wakilai uku na jam’iyyar Labour a jihar Ribas.
‘Yan takarar da aka soke sun hada da Obio/Akpor, Port Harcourt City 1 da Port Harcourt City 2 mazabar tarayya.
Jam’iyyar PDP a jihar ta garzaya kotu inda ta ce, jam’iyyar LP ba ta bi sabuwar dokar zabe ba wajen zaben ‘yan takara.
PDP dai ta roki kotun da ta soke zaben fidda gwanin da aka yi na ‘yan takarar guda uku sannan ta umurci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta soke zaben.
Mai shari’a Stephen Daylop-Pam, wanda shi ne mai shari’a a shari’ar, ya ci karo da asalin sammacin jam’iyyar PDP da ya kalubalanci cancantar jam’iyyar Labour ta tsayar da ‘yan takara a zaben fidda gwani da INEC ba ta sanya ido a kai ba.
Alkalin ya kuma ce PDP ta tabbatar da cewa INEC ba ta sanya ido a zaben fidda gwani na mazabar da abin ya shafa ba. Don haka ya umarci INEC da kada ta amince da ‘yan takarar da abin ya shafa a zaben 2023.
A halin da ake ciki, lauyan jam’iyyar Labour da ‘yan takarar uku, Uche Olewunne, ya bayyana cewa zai shawarci wadanda ke karewa da su daukaka kara kan hukuncin.