fidelitybank

Kotu ce ƙadai za ta iya sakin Nmandi Kanu – Buhari

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya tabbata da cewa, kotu ce kaɗai za ta iya sakin shugaban ƙungiyar IPOB, Nmandi Kanu.

‘Yan makonni bayan alƙawarin da ya yi wa dattawan al’ummar Ibo na duba yiwuwar sakin ɗan tawaye, Nnamdi Kanu, Buhari ya ce “ba za mu iya sakin sa ba”.

Ya ce: “Akwai sashen da ba zan iya taɓawa ba, shi ne na shari’a. Batun Kanu ya na gaban kotu. Amma abin mamakin shi ne, lokacin da ya ke Turai ya na zagin wannan gwamnati, na zaci zai so ya zo ya kare kansa daga waɗan nan zarge-zargen.

“Saboda haka muna ba shi dama ce ta kare kan sa bisa tsarinmu, ba wai ya koma Turai ya ci gaba da zaginmu ba kamar ba ɗan Najeriya ba. Ya zo nan ya soke mu…waɗanda ke cewa ya kamata a sake shi, a’a, ba zamu iya sakin sa ba.”

A watan Nuwamba ne dattawan suka gana da Buhari a Abuja, inda suka nemi ya tausaya wa jagoran na haramtacciyar ƙungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB) da ke neman kafa ƙasar Biafra a kudu maso gabashin Najeriya.

Buhari na wannan jawabin ne yayin tattaunawar sa da gidan talabijin na Channels.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp