fidelitybank

Kotu ce ƙadai za ta iya sakin Nmandi Kanu – Buhari

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya tabbata da cewa, kotu ce kaɗai za ta iya sakin shugaban ƙungiyar IPOB, Nmandi Kanu.

‘Yan makonni bayan alƙawarin da ya yi wa dattawan al’ummar Ibo na duba yiwuwar sakin ɗan tawaye, Nnamdi Kanu, Buhari ya ce “ba za mu iya sakin sa ba”.

Ya ce: “Akwai sashen da ba zan iya taɓawa ba, shi ne na shari’a. Batun Kanu ya na gaban kotu. Amma abin mamakin shi ne, lokacin da ya ke Turai ya na zagin wannan gwamnati, na zaci zai so ya zo ya kare kansa daga waɗan nan zarge-zargen.

“Saboda haka muna ba shi dama ce ta kare kan sa bisa tsarinmu, ba wai ya koma Turai ya ci gaba da zaginmu ba kamar ba ɗan Najeriya ba. Ya zo nan ya soke mu…waɗanda ke cewa ya kamata a sake shi, a’a, ba zamu iya sakin sa ba.”

A watan Nuwamba ne dattawan suka gana da Buhari a Abuja, inda suka nemi ya tausaya wa jagoran na haramtacciyar ƙungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB) da ke neman kafa ƙasar Biafra a kudu maso gabashin Najeriya.

Buhari na wannan jawabin ne yayin tattaunawar sa da gidan talabijin na Channels.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp