fidelitybank

Ba na tsoron kowanene shugaba a 2023 – Buhari

Date:

Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya ce shi bai damu da wanda zai gaje shi ba a matsayin shugaban a shekarar 2023.

Buhari ya tabbatar da hakan ne a hirarsa da kafar talabijin ta Channels TV a yammacin Laraba.

Ya bayyana cewa “Zaɓen 2023 ba matsalata ba ce”.

“Ban damu da wanda zai gaje ni ba, rabu da shi ya zo ko ma wane ne,” in ji shi.

Da ya ke amsa tambaya kan ko me ke zuwa masa a rai idan ya ji an ambaci zaɓen 2023, Buhari ya amsa da cewa: “Ba matsalata ba ce.”

Da aka tambaye shi: “Ba ka damu game da wanda zai gaje ka ba? Sai ya ce:

“Bar shi ya zo ko ma wane ne. Na tabbata na ajiye rahoton duk wani abu mai muhimmanci. Bai kamata wani ya kira ni ba da shaida a gaban kotu ba a kan wani abu, idan ba haka ba kuma zai shiga matsala.”

Buhari ya ce duk da cewa ba shi da wani ɗan takara da ya ke goyon baya a jam’iyyarsu ta APC mai mulki ya gaje shi, amma idan ya bayyana shi za a iya halaka shi.

“A’a, saboda idan na faɗa za a iya kawar da shi. Gara na bar shi a sirrance,” A cewar Buhari

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a...

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon ɗan takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...
X whatsapp