Mahukunta a Aljeriya sun rufe makarantu tsawon kwana 10 tare da kara karfafa bincike a filayen jirgin sama da kuma daukar karin matakan yaki da Korona, sakamakon karuwar masu kamuwa da cutar.
Matakin ya biyo bayan da shugaban ƙasar, Abdelmadjid Tebboune ya umarci a rufe makarantun daga ranar Alhamis a wani taron gaggawa da ministoci da manyan jami’an lafiya da kuma na tsaro suka yi.
Sai dai sanarwar da fadar shugaban kasar ta fitar ta ce ya rage ga jami’o’i su yanke shawarar ko su rufe ko kuma su sake tsarin karatunsu.
Mutane sama da 220,000 su ka kamu da korona, wanda mutane sama da 6,000 suka mutu, tun da annobar ta fara a Aljeriya.