fidelitybank

Korona: Mutane 3 sun mutu ta sanadiyar daskarewar jinni a New Zealand

Date:

A kalla mutum uku ne aka tabbatar da mutuwarsu ta sanadiyyar daskarewar jini bayan sun

Hukumar kula da ingancin allurar rigakafin COVID-19 ta kasar ce ta sanar da hakan, a ranar Litinin, inda ta ce, mutanen sun mutu ne sakamakon matsalar daskarewar jinni bayan an yi musu allurar rigakafin.

Kan wannan batun ne hukumar ta zauna, domin tattauna korafe-korafen da a ke samu, domin a gano ko su na da alaka da rigakafin ko kuma a’a.

Mutanen da suka mutu dai sun hada da wani yaro mai shekara 13, da wani matashi mai shekara 26 da kuma wani tsoho mai kimanin shekara 60.

Sai dai hukumar ta ce, ya zuwa yanzu ba ta kai ga gano alaka tsakanin allurar da daskarewar jinin a jikin tsohon mai shekara 60 ba, sannan ta na bukatar karin bayani, domin tantance rawar da rigakafin ta taka a mutuwar yaron mai shekara 13.

Sanarwar ta kuma kara da cear, bisa ga bayanan da su ka tattara, sun gano cewa daskarewar jinin ta faru ne a jikin wannan matashin mai shekara 26 sakamakon rigakafin.

Rahotanni dai sun ce matashin ya fara nuna alamun cutar ne ’yan kwanaki kadan da yi masa rigakafin, sannan ya mutu cikin mako biyu da karbar zagaye na farko na allurar.

Hukumar dai ta amince cewa matsalar ta daskarewar jini na daga cikin illolin da a ka fi fuskanta daga rigakafin na Pfizer, amma ta ce ita kanta COVID-19 din na iya haifar da matsalar daskarewar jinin. A cewar kamfanin dillancin labarai na NAN.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuÉ—in...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaÉ—an wajen tsaron Æ™asa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haÉ—in...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...
X whatsapp