A kalla mutum uku ne aka tabbatar da mutuwarsu ta sanadiyyar daskarewar jini bayan sun
Hukumar kula da ingancin allurar rigakafin COVID-19 ta kasar ce ta sanar da hakan, a ranar Litinin, inda ta ce, mutanen sun mutu ne sakamakon matsalar daskarewar jinni bayan an yi musu allurar rigakafin.
Kan wannan batun ne hukumar ta zauna, domin tattauna korafe-korafen da a ke samu, domin a gano ko su na da alaka da rigakafin ko kuma a’a.
Mutanen da suka mutu dai sun hada da wani yaro mai shekara 13, da wani matashi mai shekara 26 da kuma wani tsoho mai kimanin shekara 60.
Sai dai hukumar ta ce, ya zuwa yanzu ba ta kai ga gano alaka tsakanin allurar da daskarewar jinin a jikin tsohon mai shekara 60 ba, sannan ta na bukatar karin bayani, domin tantance rawar da rigakafin ta taka a mutuwar yaron mai shekara 13.
Sanarwar ta kuma kara da cear, bisa ga bayanan da su ka tattara, sun gano cewa daskarewar jinin ta faru ne a jikin wannan matashin mai shekara 26 sakamakon rigakafin.
Rahotanni dai sun ce matashin ya fara nuna alamun cutar ne ’yan kwanaki kadan da yi masa rigakafin, sannan ya mutu cikin mako biyu da karbar zagaye na farko na allurar.
Hukumar dai ta amince cewa matsalar ta daskarewar jini na daga cikin illolin da a ka fi fuskanta daga rigakafin na Pfizer, amma ta ce ita kanta COVID-19 din na iya haifar da matsalar daskarewar jinin. A cewar kamfanin dillancin labarai na NAN.