Koriya ta Arewa ta harba makami mai linzami a gabar tekun gabashin kasar, gwajin makami mai linzami na bakwai cikin wata guda kuma mafi girma cikin shekaru biyar da ta yi.
Gwamnatin Japan ta ce gwajin makamin ya yi tafiya mai tsirin kilomita dubu biyu kafin ya fada tekun Japan mai nisan kilomita dari takwas daga wurin da aka harba makamin.
Shugaban Koriya ta Kudu, Moon Jae-in, ya kira taron kwamitin tsaro na gaggawa a karon farko, tun cikin shekara guda, inda ya shaida musu cewa, Korya Ta Arewa, ta wuce makadi da rawa.
To sai dai shugaban Koriya Ta Arewar, Kim Jong Un, ya yi kira ga dakarunsa, su hanzarta bunkasa fasaharsu da karfinsu, tare da yin watsi da kiran da Amurka ta yi na tattaunawa kan kawar da makaman nukiliya.