fidelitybank

Kirsimeti: ‘Yan Shi’a sun halarci coci a Zaria

Date:

Mabiya addinin shi’a sun ziyarci majami’ar mabiya addinin Kirista, domin halartar bukukuwan Kirsimieti.

Da ya ke jawabi a wata hira da manema labarai jim kadan bayan kammala hidimar, shugaban kungiyar, Farfesa Isa Mshelgaru ya ce, makasudin halartar taron shi ne bunkasa soyayya, hakuri da fahimtar juna a tsakanin ‘yan Najeriya.

Ya ce, “Mun yanke shawarar halartar wannan hidimar coci, domin yau ce ranar Kirsimeti, ranar da ake bikin zagayowar ranar haihuwar Yesu a dukan duniya, kuma muna jin cewa muna son mu gaya musu abubuwan da su ka ji a ranar haihuwar sa.

“Zuwan Yesu duniya albarka ce ga kowa da kowa, domin haka muna fata mu zo mu yi bikin wannan rana mai daraja tare da su.”

Ya ce a matsayin su na musulmi suna daukar kiristoci a matsayin ’yan uwansu a cikin bil’adama, ya na mai jaddada cewa, suna hidimar cocin ne, domin hada kai da su wajen gudanar da bukukuwa da kuma raba musu farin cikin wannan rana.

“Wannan ya na da mahimmanci a yanzu da kasar ke fuskantar kalubalen tsaro da yawa wadanda ke bukatar dukkan hannaye su kasance a kan wasu, domin shawo kan su,” inji shi.

A sakonsa ga sauran ‘yan Najeriya, Mshelgaru ya shawarci ‘yan Nijeriya su hadu ba tare da la’akari da bambancin addini ko kabilanci ko siyasa ba, domin ceto al’ummar kasar baki daya.

 

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp