Ma’aikatar Lafiya ta Zirin Gaza ta yi gargaɗin cewa awa 48 kacal suka rage kafin dukkan kayayyakin aikin lafiyar da take da su su ƙare a yankin sakamakon datse hanyoyin shiga da fita da Isra’ila ta yi.
Sanarwar da ta fitar na cewa ba za ta iya ci gaba da ayyuka a asibitoci ba saboda tashar lantarki tilo da take bai wa Gaza wuta ta rufe saboda rashin man fetur da take fama da shi.
Yanzu haka asibitocin na aiki ne da ƙananan injinan lantarki, waɗanda ke fama da ƙarancin man su ma.
Ya zuwa yanzu, ma’aikatar lafiyar ta ce, an jikkata Falasɗinawa 215, yayin da jiragen Isra’ilar ke ci gaba da ruwan wuta a kan unguwannin Gaza.
Isra’ila ta ce tana harar mayaƙan ƙungiyar Palestinian Islamic Jihad ne, amma hare-haren sun kashe fararen hula 32 zuwa yanzu. In ji BBC.