Sabon zaɓaɓɓen mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya kai wa tsofaffin shugabanni, Ibrahim Badamasi Babangida da kuma Abdulsalami Abubakar ziyara a Minna, babban birnin jihar Neja.
Shettima ya kwatanta tsoffin shugabannin a matsayin mutanen dattaku da kuma ubannin ƙasa, inda ya ce gwamnati mai zuwa za ta yi aiki da su domin ciyar da ƙasar gaba.

Daga bisani kuma ya jagoranci tawagarsa wajen kai gaisuwa ga Sarkin Minna Dakta Umar Farouq Bahago, inda aka yi addu’o’i don samun zaman lafiyar ƙasa. In ji BBC.