Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri na hallaka jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ba zai rura wutar rikicin da ake yi yanzu ba, hasali zai ma kawo karshen rikicin ne.
A wata tattaunawa da tashar talabijin ta ABC ta Amurka ta yi da shi ne Netanyahu ya bayyana haka.
A yayin hirar duk wata tambaya da aka yi masa game da ko Isra’ila na shirin kashe babban jagoran addinin, Netanyahu ya ki kawar da yuwuwar hakan.
Da aka matsa shi a kan ko za su hari jagoran, sai ya ce : ”Muna yin abin da muke da bukatar yi.”
“Mun hari manyan masana nukiliyarsu,” ya kara da cewa. “Har yanzu muna da sauran aikin da za mu yi a daya bangaren.”
Haka kuma jagoran na Isra’ila ya nuna cewa sun kai wa Iran hari ne domin kare al’umma, domin kare duk wata barazanar nukiliya daga Iran.
“Yau birnin Tel Aviv, ne gobe kuma New York, ne ” in ji shi.