fidelitybank

Kasafin Kudi: El-Rufa’I zai kashe Naira biliyan 6 a manyan asibitoci

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai’s ya ware Naira biliyan 6, domin inganta kayan aiki ga manyan asibitoci a fadin jihar Kaduna a shekarar 2022.

Hakan ya nuna cewa cikin kasafin kudin 2022 na Naira biliyan 278.6 da El’-Rufa’I ya sanyawa hannu.

A cikin kasafin kudin na 2022 na Naira biliyan 278.6, za a kashe Naira biliyan 15.7 ga ma’aikatar lafiya, inda za a kashe Naira biliyan 7.4 wajen gina da kuma samar da kayan aikin asibitin kwararru mai gadaje 300.

Gwamnatin Kaduna ta kuma ware Naira miliyan 51.6, domin ginawa tare da gyara bangaren karbar agajin gaggawa na manyan asibitocin Kafanchan da Saminaka da Birnin Gwari da Hajiya Gambo Sawaba.

Kasafin kudin ya kuma hada da gina sabuwar kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma a Pambegua, wadda za ta samu Naira miliyan 281.7.

Takardar ta nuna an ware Naira miliyan 17.4 domin samar da firinjin adana jini guda 20.

Takardar ta kuma nuna cewa an ware Naira miliyan 370, domin gina cibiyar kula da masu fama da rauni a Doka, yayin da a ka ware Naira miliyan 28.9, domin kula da kayan aikin jinya a cibiyoyin lafiya na matakan lafiya a farko 31.

Sannan ya nuna cewa an ware Naira miliyan 861.7 a matsayin takwaran aikinsa na shirin yaki da cutar zazzabin cizon sauro, domin karfafa tsarin rigakafi da abbatar da inganci da kula da ingancin tantance cutar zazzabin cizon sauro da magani.

Hakazalika, za a kashe Naira miliyan 62.6 kan cutar tarin fuka mai jure wa magunguna, Naira miliyan 188 kan shirin samar da abinci mai gina jiki na gaggawa na Kaduna da kuma Naira miliyan 50 a karkashin tallafin samar da abinci mai gina jiki da bankin duniya ke tallafawa a Najeriya.

 

 

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp