Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai’s ya ware Naira biliyan 6, domin inganta kayan aiki ga manyan asibitoci a fadin jihar Kaduna a shekarar 2022.
Hakan ya nuna cewa cikin kasafin kudin 2022 na Naira biliyan 278.6 da El’-Rufa’I ya sanyawa hannu.
A cikin kasafin kudin na 2022 na Naira biliyan 278.6, za a kashe Naira biliyan 15.7 ga ma’aikatar lafiya, inda za a kashe Naira biliyan 7.4 wajen gina da kuma samar da kayan aikin asibitin kwararru mai gadaje 300.
Gwamnatin Kaduna ta kuma ware Naira miliyan 51.6, domin ginawa tare da gyara bangaren karbar agajin gaggawa na manyan asibitocin Kafanchan da Saminaka da Birnin Gwari da Hajiya Gambo Sawaba.
Kasafin kudin ya kuma hada da gina sabuwar kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma a Pambegua, wadda za ta samu Naira miliyan 281.7.
Takardar ta nuna an ware Naira miliyan 17.4 domin samar da firinjin adana jini guda 20.
Takardar ta kuma nuna cewa an ware Naira miliyan 370, domin gina cibiyar kula da masu fama da rauni a Doka, yayin da a ka ware Naira miliyan 28.9, domin kula da kayan aikin jinya a cibiyoyin lafiya na matakan lafiya a farko 31.
Sannan ya nuna cewa an ware Naira miliyan 861.7 a matsayin takwaran aikinsa na shirin yaki da cutar zazzabin cizon sauro, domin karfafa tsarin rigakafi da abbatar da inganci da kula da ingancin tantance cutar zazzabin cizon sauro da magani.
Hakazalika, za a kashe Naira miliyan 62.6 kan cutar tarin fuka mai jure wa magunguna, Naira miliyan 188 kan shirin samar da abinci mai gina jiki na gaggawa na Kaduna da kuma Naira miliyan 50 a karkashin tallafin samar da abinci mai gina jiki da bankin duniya ke tallafawa a Najeriya.