fidelitybank

Kasafin Kudi: El-Rufa’I zai kashe Naira biliyan 6 a manyan asibitoci

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai’s ya ware Naira biliyan 6, domin inganta kayan aiki ga manyan asibitoci a fadin jihar Kaduna a shekarar 2022.

Hakan ya nuna cewa cikin kasafin kudin 2022 na Naira biliyan 278.6 da El’-Rufa’I ya sanyawa hannu.

A cikin kasafin kudin na 2022 na Naira biliyan 278.6, za a kashe Naira biliyan 15.7 ga ma’aikatar lafiya, inda za a kashe Naira biliyan 7.4 wajen gina da kuma samar da kayan aikin asibitin kwararru mai gadaje 300.

Gwamnatin Kaduna ta kuma ware Naira miliyan 51.6, domin ginawa tare da gyara bangaren karbar agajin gaggawa na manyan asibitocin Kafanchan da Saminaka da Birnin Gwari da Hajiya Gambo Sawaba.

Kasafin kudin ya kuma hada da gina sabuwar kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma a Pambegua, wadda za ta samu Naira miliyan 281.7.

Takardar ta nuna an ware Naira miliyan 17.4 domin samar da firinjin adana jini guda 20.

Takardar ta kuma nuna cewa an ware Naira miliyan 370, domin gina cibiyar kula da masu fama da rauni a Doka, yayin da a ka ware Naira miliyan 28.9, domin kula da kayan aikin jinya a cibiyoyin lafiya na matakan lafiya a farko 31.

Sannan ya nuna cewa an ware Naira miliyan 861.7 a matsayin takwaran aikinsa na shirin yaki da cutar zazzabin cizon sauro, domin karfafa tsarin rigakafi da abbatar da inganci da kula da ingancin tantance cutar zazzabin cizon sauro da magani.

Hakazalika, za a kashe Naira miliyan 62.6 kan cutar tarin fuka mai jure wa magunguna, Naira miliyan 188 kan shirin samar da abinci mai gina jiki na gaggawa na Kaduna da kuma Naira miliyan 50 a karkashin tallafin samar da abinci mai gina jiki da bankin duniya ke tallafawa a Najeriya.

 

 

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...
X whatsapp