fidelitybank

Kasafin Kudi: El-Rufa’I zai kashe Naira biliyan 6 a manyan asibitoci

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai’s ya ware Naira biliyan 6, domin inganta kayan aiki ga manyan asibitoci a fadin jihar Kaduna a shekarar 2022.

Hakan ya nuna cewa cikin kasafin kudin 2022 na Naira biliyan 278.6 da El’-Rufa’I ya sanyawa hannu.

A cikin kasafin kudin na 2022 na Naira biliyan 278.6, za a kashe Naira biliyan 15.7 ga ma’aikatar lafiya, inda za a kashe Naira biliyan 7.4 wajen gina da kuma samar da kayan aikin asibitin kwararru mai gadaje 300.

Gwamnatin Kaduna ta kuma ware Naira miliyan 51.6, domin ginawa tare da gyara bangaren karbar agajin gaggawa na manyan asibitocin Kafanchan da Saminaka da Birnin Gwari da Hajiya Gambo Sawaba.

Kasafin kudin ya kuma hada da gina sabuwar kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma a Pambegua, wadda za ta samu Naira miliyan 281.7.

Takardar ta nuna an ware Naira miliyan 17.4 domin samar da firinjin adana jini guda 20.

Takardar ta kuma nuna cewa an ware Naira miliyan 370, domin gina cibiyar kula da masu fama da rauni a Doka, yayin da a ka ware Naira miliyan 28.9, domin kula da kayan aikin jinya a cibiyoyin lafiya na matakan lafiya a farko 31.

Sannan ya nuna cewa an ware Naira miliyan 861.7 a matsayin takwaran aikinsa na shirin yaki da cutar zazzabin cizon sauro, domin karfafa tsarin rigakafi da abbatar da inganci da kula da ingancin tantance cutar zazzabin cizon sauro da magani.

Hakazalika, za a kashe Naira miliyan 62.6 kan cutar tarin fuka mai jure wa magunguna, Naira miliyan 188 kan shirin samar da abinci mai gina jiki na gaggawa na Kaduna da kuma Naira miliyan 50 a karkashin tallafin samar da abinci mai gina jiki da bankin duniya ke tallafawa a Najeriya.

 

 

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp