Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya sanya hannu a kan kasafin kudin shekarar 2022 zunzurutun kudi fiye da Naira biliyan 221.
Ganduje ya sanya hannu ne bayan da majalisar dokokin jihar Kano ta kammala gyare-gyaren ta.
Ya ce”Kunshin kasafin kudin zai sa ya kammala manyan ayyuka, domin ganin gwamnati mai zuwa ba ta gaji bashi ba”.
Sai dai shugaban majalisar dokokin Kano, HamIsu Ibrahim Chidari ya ce, kunshin kasafin a bana ya samu kari.