fidelitybank

KAROTA ta rage kudin rijistar ‘yan Adaidaita Sahu

Date:

Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta rage wa direbobin baburara masu taya uku wanda aka fi sani da Adaidaita Sahu kuɗin sabunta takardar shaidar izinin tuƙi daga Naira 8,000 zuwa Naira 5,000.

Mai magana da yawun hukumar, Nabilusi Abubakar Ƙofar Na’isa ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.

Tun a ranar 10 ga watan Janairu, 2022 ne direbobin baburaran Adaidaita Sahu suka tsunduma yajin aikin gargaɗi, sakamakon rashin amincewarsu da biyan Naira 8,000 a matsayin kuɗin sabunta takardar shaidar izinin tuƙin da kuma sauran batutuwa.

Hukumar ta ce, ta kuma rage kuɗin sabuwar izinin tuƙi daga Naira 18,000 zuwa Naira 1,500.

Wannan matakin ya biyo baya ne, tun kammala wani zaman sulhu da ta yi da lauyoyin direbobin baburaran Barista Abba Hikima Fagge.

Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi ta Jihar Kano, Aminu Sani Gadanya ne ya jagoranci lauyoyi a wajen zaman sulhun.

A cewar KAROTA, matuƙa baburan za su biya waɗannan kuɗaɗe ne daga nan zuwa ƙarshen watan Fabrairu, 2022.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp