Tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya, ya gargadi gwamnatin tarayya kan yunkurinta na kara farashin man fetur.
Abdulsalami ya yi gargadin ne bayan kara farashin litar man fetur zuwa Naira 302, wanda tuni ya sanya kungiyoyin kwadago za su shiga zanga-zanga.
Da ya ke bayanin nasa a wurin babban taron tattaunawa na Daily Trust karo na 19 a ranar Alhamis, 20 ga Janairu, 2022 a Abuja.
Abdulsalami, ya ce, “Karin farashin man zai jefa karin ’yan Najeriya a cikin talauci”.
Duk da cewa kwamitin wanda mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo, ya ke jagoranta ya bayar da shawarar kara farashin a watan Nuwamba, a halin yanzu dai farashin man fetur ya na a kan Naira 162 zuwa Naira 165 ne a Najeriya.
Yunkurin kara farashin man na daga cikin matakan da gwamnatin tarayya take dauka na janye hannunta a harkar gudanar da bangaren man fetur da kuma bayar da tallafi a kansa.