fidelitybank

Nan da watan Maris zamu kammala tashar shigo da kaya a Kano – Bawuro

Date:

Shugaban tashar sauke kayayyaykin da ake shigo da su tsandauri ta Dala Inland Dry Port, Abubakar Bawuro, ya ce, kasuwanci tsakanin Najeriya da makwabciyarta ta Arewa, Jamhuriyar Nijar za ta samu ci gaba mai tarin yawa yayin da ake sa ran kaddamar da tashar a jihar Kano cikin watan Maris na 2022.

Ya ce, aikin wanda kawo yanzu ya lakume sama da Naira biliyan 5 na gine-gine ya kai sama da kashi 80 bisa 100 da aka kammala, tare da sauran ayyukan da ake sa ran za a yi nan da karshen watan Fabrairu na shirye-shiryen fara tashi.

Ya yin tattaunawa da magana labarai, a lokacin da ya ziyarci Sakataren zartarwa na Hukumar Kula da Jiragen Ruwa ta Najeriya (NSC), Mista Emmanuel Jime a Abuja.

A cewar Bawuro, “Muhimman wuraren ginin da suka hada da wurin da aka tara kwantenan tashohin ruwa a dakunan ajiyar kaya da guraben aikin gudanarwa da hanyoyin shiga da kuma samar da wutar lantarki a tashar, an yi su sosai. Idan ka duba su a ka tantance su gaba daya, za mu iya aminta da cewa mun kai sama da kashi 80 cikin 100 na kammalawa.

“Muna so mu tabbatar muku da cewa za mu yi aiki cikin awanni 24 a mako guda, domin ganin mun cimma burin ganin mun tabbatar da kuma kaddamar da tashar a karshen watan Maris”. In ji Bawuro.

Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Najeriya, Mista Emmanuel Jime, ya yi alkawarin bayar da duk wani goyon bayan da ya dace, domin tabbatar da nasarar IDP na Dala.

 

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu...

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...
X whatsapp