Wani dan majalisar dokokin Ghana, Patrick Boamah, ya bukaci al’ummar kasar da su yi watsi da wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya da za su yi da Najeriya a shekarar 2022.
Ghana za ta kara da Najeriya a watan Maris a wasan gurbin cancantar shiga gasar cin kofin duniya da za a gudanar a kasar Qatar na 2022.
Boamah ya ce“Kar Ghana ta bata lokacinta da Najeriya, wanda kungiyar ta Super Egles ta fi Black Stars kyau da iya taka leda”.
“Idan akwai bukata, ya kamata mu rusa kungiyarmu ta kasar mu shirya kungiya cikin shekaru biyar masu zuwa,” in ji Boamah a zauren majalisar, a cewar Citi Sports via Goal.
“Kada mu bata lokacinmu da Najeriya a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya na gaba.
“Ku dubi tawagar da Najeriya ke da su, duk da cewa an fitar da su a gasar, amma ba na tunanin da wannan tsarin da muke da shi, za mu iya jurewa ‘yan Najeriya.”
Black Stars dai ba su taka wata rawar gani ba a gasar cin kofin nahiyar Afrika da ake gudanarwa a kasar Kamaru.