fidelitybank

Kano Pillars ta kwashi kashin ta a hannun Ikorodu City

Date:

Ikorodu City ta doke Kano Pillars 4-1 a wasan mako na 20 a gasar Premier ta Najeriya da suka kara ranar Laraba a Legas.

Ikorodu City ta fara cin ƙwallo a minti na biyu da take leda ta hannun Adelani Shola, sannan ta kara na biyu ta hannun Uzondu Harrison a minti na 27.

Daf da za su je hutu ne Pillars ta zare ɗaya ta hannun Abba Adam, kuma na huɗu da ya zura a raga a kakar nan.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne mai masaukin baƙi ta kara na uku, bayan da Pillars ta ci gida a kwana daga Harrison Austin, sannan Ayomide Cole ya ci na huɗu.

Tun a ranar Talata da sanyin safiya Pillars ta ziyarci Legas a jirgin sama a karon farko da gwamnati ta yi wannan bajintar a kakar nan.

Ta kuma yi haka ne domin ƴan wasa su samu natsuwa da hutun da suke bukata, domin buga wasa da Ikorodu, sannan su koma Kano a kan kari don fuskantar wani kalubale ranar Lahadi.

Ranar 8 ga watan Satumba, Pillars ta caskara Ikorodu City 3-0 a wasan farko na fara kakar bana da suka fafata a filin wasa na Muhammadu Dikko a jihar Katsina.

Ranar Lahadi 2 ga watan Fabrairu, Kano Pillars za ta karɓi bakuncin Bayelsa United, ita kuwa Ikorodu City za ta je Enugu Rangers.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp