fidelitybank

Kano Pillars ta kwashi kashin ta a hannun Ikorodu City

Date:

Ikorodu City ta doke Kano Pillars 4-1 a wasan mako na 20 a gasar Premier ta Najeriya da suka kara ranar Laraba a Legas.

Ikorodu City ta fara cin ƙwallo a minti na biyu da take leda ta hannun Adelani Shola, sannan ta kara na biyu ta hannun Uzondu Harrison a minti na 27.

Daf da za su je hutu ne Pillars ta zare ɗaya ta hannun Abba Adam, kuma na huɗu da ya zura a raga a kakar nan.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne mai masaukin baƙi ta kara na uku, bayan da Pillars ta ci gida a kwana daga Harrison Austin, sannan Ayomide Cole ya ci na huɗu.

Tun a ranar Talata da sanyin safiya Pillars ta ziyarci Legas a jirgin sama a karon farko da gwamnati ta yi wannan bajintar a kakar nan.

Ta kuma yi haka ne domin ƴan wasa su samu natsuwa da hutun da suke bukata, domin buga wasa da Ikorodu, sannan su koma Kano a kan kari don fuskantar wani kalubale ranar Lahadi.

Ranar 8 ga watan Satumba, Pillars ta caskara Ikorodu City 3-0 a wasan farko na fara kakar bana da suka fafata a filin wasa na Muhammadu Dikko a jihar Katsina.

Ranar Lahadi 2 ga watan Fabrairu, Kano Pillars za ta karɓi bakuncin Bayelsa United, ita kuwa Ikorodu City za ta je Enugu Rangers.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp