fidelitybank

Kano: EFCC ta kama matasa Uku da katin ATM 1,144

Date:

Hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC), ta kama wasu mutane Uku da ake zargi a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano (MAKIA), a lokacin da suke kokarin safarar katinan kudi na ATM 1,144 zuwa kasar waje.

Mai magana da yawun hukumar, Wilson Uwujaren, ya ce wadanda ake zargin akwai, Abdullahi Usman da Musa Abubakar da kuma Abdulwahid Auwalu, an kuma kama su ne tsakanin ranar 24 ga watan Nuwamba zuwa 1 ga Disamba, 2021 ta hannun jami’an ofishin hukumar na jihar Kano.

An gano cewa Abubakar da ke kan hanyarsa ta zuwa kasar hadadiyar daular larabawa Dubai, ya boye katin ATM guda 714, yayin da Usman da ke kan hanyarsa ta zuwa Saudiyya, ya na da katin ATM guda 298 a hannunsa.

A daya bangaren kuma, an kama Auwalu da katin ATM 132 a lokacin da yake kokarin shiga jirgin kasar Habasha zuwa birnin Santanbul na kasar Turkiyya.

Hukumar EFCC ta ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a kotu da zarar ta kammala binciken ta.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

MuÆ™arraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon É—an majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp