fidelitybank

Kannywood: Ban cinye kudin kowa ba – Sadik Sani Sadik

Date:

Kotun shari’ar musulunci da ke Hotoro Masallacin Juma’a a Jihar Kano, ta bayar da umarnin a kamo mata shahararren jarumin fina-finan Hausa na Kannywood a Najeriya, Sadiq Sani Sadiq, bisa zargin saɓa alƙawari da ya yi.

Tun da farko wani mai shirya fina-finai, Aliyu Muhammad Hannas ne ya shigar da ƙarar a gaban kotun, inda ya ke ƙorafin cewar ya baiwa jarumin kuɗi domin ya yi masa aikin film, amma yaƙi zuwa don yin aikin.

Mai ƙarar ya kuma yi ƙorafin cewa ƙin yi aikin da Sadiq ya yi ya ja masa asara mai yawa.

Alkalin Kotun, Maishari’a Sagiru Adamu, yace Sadiq ya bijirewa umarnin kotu duk da sammacin da aka bashi, tare da liƙe masa sammacin a bangon gidansa, amma yaki halartar zaman kotun.
Wanda hakan ne ya sanya alkalin ya baiwa jami’an ƴan sandan kotun umarnin kamo jarumin a duk inda ya ke zuwa gaban kotun.

Haka kuma ko tun ta ce da zarar an kamo jarumin masana’antar Kanywood ɗin za a cigaba da zaman sauraren shari’ar.

Da ya ke zantawa da manema labarai, Sadiq ya ce ba mai shirya fim ɗin ba ne ya bashi kuɗin kai tsaye ba.

Sadiq ya ƙara da cewa Naira dubu ɗari a ka bashi a matsayin wani ɓangare na kuɗin kwantaragin fim ɗin.

In da ya ce, shi ba cinye masa kuɗi ya yi ba, hasali ma bai san ko wanene mai fim ɗin ba, tunda ba kai tsaye su ka kulla yarjejeniyar ba.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp