fidelitybank

Kannywood: Ban cinye kudin kowa ba – Sadik Sani Sadik

Date:

Kotun shari’ar musulunci da ke Hotoro Masallacin Juma’a a Jihar Kano, ta bayar da umarnin a kamo mata shahararren jarumin fina-finan Hausa na Kannywood a Najeriya, Sadiq Sani Sadiq, bisa zargin saɓa alƙawari da ya yi.

Tun da farko wani mai shirya fina-finai, Aliyu Muhammad Hannas ne ya shigar da ƙarar a gaban kotun, inda ya ke ƙorafin cewar ya baiwa jarumin kuɗi domin ya yi masa aikin film, amma yaƙi zuwa don yin aikin.

Mai ƙarar ya kuma yi ƙorafin cewa ƙin yi aikin da Sadiq ya yi ya ja masa asara mai yawa.

Alkalin Kotun, Maishari’a Sagiru Adamu, yace Sadiq ya bijirewa umarnin kotu duk da sammacin da aka bashi, tare da liƙe masa sammacin a bangon gidansa, amma yaki halartar zaman kotun.
Wanda hakan ne ya sanya alkalin ya baiwa jami’an ƴan sandan kotun umarnin kamo jarumin a duk inda ya ke zuwa gaban kotun.

Haka kuma ko tun ta ce da zarar an kamo jarumin masana’antar Kanywood ɗin za a cigaba da zaman sauraren shari’ar.

Da ya ke zantawa da manema labarai, Sadiq ya ce ba mai shirya fim ɗin ba ne ya bashi kuɗin kai tsaye ba.

Sadiq ya ƙara da cewa Naira dubu ɗari a ka bashi a matsayin wani ɓangare na kuɗin kwantaragin fim ɗin.

In da ya ce, shi ba cinye masa kuɗi ya yi ba, hasali ma bai san ko wanene mai fim ɗin ba, tunda ba kai tsaye su ka kulla yarjejeniyar ba.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp