Rahotanni daga jihar Kaduna na nuni da cewa wasu ‘yan bindiga da aka fi sani da ‘yan ta’adda sun kai hari kauyen Unguwan Gimbiya da ke jihar sun kuma kashe mutane biyu tare dayin garkuwa da mutane akalla 50.
Political Nigeria ta rawaito cewa, ‘yan bindigar sun kai hari da sanyin safiyar Juma’a.
Wannan dai bas hi ne karo na farko ba da ‘yan ta’addar ke kai irin wannan harin ba a yankin, wanda hakan ne ya sanya gwamnatin tarayya ta ayyana ‘yan bindigar a matsayin ‘yan ya’adda.