Matsalar garkuwa da mutane na ci gaba da tayar da hankulan jama’a a Arewacin Najeriya. Lamarin da ya fi ta’azzara a jihohin Arewa maso Yamma irin su Zamfara da Katsina da Kaduna.
Sai dai hankulan jama’a na ƙara karkata kan titin Kaduna zuwa Abuja, sakamakon sace mutanen da har yanzu ba a san adadinsu ba, da kuma kashe wani tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Zamfara Alhaji Sagir Hamidu.
A baya a na ta murna cewa an samu saukin matsalar garkuwa da mutane a wannan shahararriyar hanya.
Hukumomin Najeriya sun ɗauki matakan kariya tare masu yawa da suka hada da girke sojoji masu yawa ciki har da wasu sojoji mata da suke sintiri a kan titin. Masana harkokin tsaron sun ce wadannan matakai sun yi matukar tasiri a zahiri, amma kuma abin da ya faru a karshe makon jiya ƙara tayar da hankulan al’ummar kasar.
Bayanai sun nuna cewa akwai garuruwa Uku da masu garkuwa da mutane suka fi cin karensu babu babbaka a wannan yankin garuruwan su ne Jere da Katari da kuma Rijana.
Malam Kabiru Adamu shi ne shugaban kamfanin Becon Consultancy da ke nazari kan harkokin tsaro a Najeriya, kuma ya shaida wa BBC cewa akwai dalilai guda Uku da suka sanya masu garkuwa da mutane suke yawan tare mutane a wadannan garuruwa.
“Babu wasu kwararan bincike da aka gudanar a ƙasa, amma abin da ya bayyana a zahiri shi ne wadannan ƙauyuka na da dazuka da tsaunuka ga kuma ruwa a gefensu,” inji shi.