fidelitybank

Kaduna-Abuja: An fi yin garkuwa a kan hanyar Jere da Katari da Rijana – Bincike

Date:

Matsalar garkuwa da mutane na ci gaba da tayar da hankulan jama’a a Arewacin Najeriya. Lamarin da ya fi ta’azzara a jihohin Arewa maso Yamma irin su Zamfara da Katsina da Kaduna.

Sai dai hankulan jama’a na ƙara karkata kan titin Kaduna zuwa Abuja, sakamakon sace mutanen da har yanzu ba a san adadinsu ba, da kuma kashe wani tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Zamfara Alhaji Sagir Hamidu.

A baya a na ta murna cewa an samu saukin matsalar garkuwa da mutane a wannan shahararriyar hanya.

Hukumomin Najeriya sun ɗauki matakan kariya tare masu yawa da suka hada da girke sojoji masu yawa ciki har da wasu sojoji mata da suke sintiri a kan titin. Masana harkokin tsaron sun ce wadannan matakai sun yi matukar tasiri a zahiri, amma kuma abin da ya faru a karshe makon jiya ƙara tayar da hankulan al’ummar kasar.

Bayanai sun nuna cewa akwai garuruwa Uku da masu garkuwa da mutane suka fi cin karensu babu babbaka a wannan yankin garuruwan su ne Jere da Katari da kuma Rijana.

Malam Kabiru Adamu shi ne shugaban kamfanin Becon Consultancy da ke nazari kan harkokin tsaro a Najeriya, kuma ya shaida wa BBC cewa akwai dalilai guda Uku da suka sanya masu garkuwa da mutane suke yawan tare mutane a wadannan garuruwa.

“Babu wasu kwararan bincike da aka gudanar a ƙasa, amma abin da ya bayyana a zahiri shi ne wadannan ƙauyuka na da dazuka da tsaunuka ga kuma ruwa a gefensu,” inji shi.

 

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp