fidelitybank

Kabilar Igbo ta zargi EFCC a kan kamun mutanen ta ‘yan takara

Date:

Kungiyar al’adun kabilar Igbo ta Apex, Ohanaeze Ndigbo, ta zargi hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, da mayar da kanta a matsayin wani shiri na musgunawa mutanen Kudu-maso-Gabas a zaben shugaban kasa na 2023.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar Ohanaeze Ndigbo Youth Council Worldwide, OYC, Mazi Okwu Nnabuike ya fitar ranar Talata.

Okwu, wanda ya yabawa tsohon gwamnan Imo, Sanata Rochas Okorocha kan shiga takarar shugaban kasa, ya ce, ya zama ruwan dare hukumar EFCC ta bi mutanen yankin Kudu maso Gabas da zarar sun nuna sha’awarsu ta tsayawa takarar shugaban kasa.

A ranar Litinin ne hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa ta shigar da kara a gaban kotu kan tuhume-tuhume 17 a kan Okorocha, bisa zargin wawure kimanin Naira biliyan 2.9 a matsayin gwamna.

Da take mayar da martani, kungiyar ta OYC ta shawarci hukumar EFCC da kada ta koma cikin irin lokacin mulkin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, inda ake amfani da hukumar wajen tsoratar da duk ‘yan siyasar adawa.

 

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp