fidelitybank

Jita-Jita: Da gaske ne Aisha Buhari ta na da juna biyu?

Date:

Sabbin Hotunan Uwargidan Shugaban Najeriya, A’isha Buhari na kara rura wutar jita-jitar da ke ta bazuwa na daukar ciki a fadin kasar, inda ‘yan Najeriya ke tunanin ko da gaske cewa za ta haihu.

People’s Gazette ta rawaito cewa daya daga cikin hotunan da jaridar ta fitar ta ce, Aisha Buhari tare da mijinta, shugaban kasa Muhamadu Buhari, sun kewaye jami’an tsaro, daya daga cikinsu dauke da jakar hannu.

A cikin wata kaftan lace mai launin rawaya da bakar abun rufa da aka lullube da abin da ya zama kamar na jariri, wanda Aisha Buhari mai shekaru 50 ta dora hannunta na dama a kan cikin ta.

A cewar jaridar mutane na ta tofa albarkacin bakin su a kan wannan batu, domin kuwa wani hoto ya nuna ma’auratan farko suna zaune a cikin jirgin sama. Wani zuzzurfan tunani da a ka yi wa Aisha Buhari ya nuna cikakkiyar fuska irin ta mace mai juna biyu, daban da na baya da a ka saba.

Hoto na uku ya nuna ma’auratan a kan matakalar jirgin, da alamun jinjiri yayin da uwargidan shugaban kasar ta sauka a hankali.

Kalamun da ke ta mayar da martani daga shafukan sada zumunta na cewa, “Aisha Buhari ta na da ciki ko abin da ke cikinta,” inji wani mai amfani da shafin Twitter @Promise.

Shi ma wani mai amfani da shafin Twitter, @Solowizzy ya yi tsokaci a kan hotunan, inda ya ce, “Yan Najeriya me ku ke tunani kan wadannan hotuna? Babu shakka Aisha Buhari na da ciki.”

A wani sako mai ban dariya da ya wallafa a shafinsa na Twitter, @Alamin97296003 ya taya Buhari mai shekaru 79 murna kan “kwazonsa”.

“Aisha Buhari ta na da ciki. Baba Buhari mai aiki tukuru,” inji mai amfani da Twitter.

Idan ta na da ciki, Mrs Buhari, wacce ta riga ta zama kaka, za ta kasance matar shugaban kasa ta farko da a ka san ta na da juna biyu a lokacin da mijinta ke kan mulki, kuma mai yiwuwa ita ce ta fara haihuwa a fadar shugaban kasa.

Tun a shekarar 2016 ne a ka fara fitowa fili cewa Aisha Buhari ba ta ji dadin yadda mijinta ke tafiyar da al’amuran kasar nan ba. A wata hira da ta yi da sashen Hausa na BBC, ta yi ikirarin cewa an sace gwamnatin Buhari.

A cewar rahoton na Fabrairu, ta ziyarci Daura tare da Buhari a ranar 9 ga Maris, 2019, a lokacin zaben shugaban kasa.

A wani martani da Aisha Buhari ta ce,”Shugaban kasa bai san 45 daga cikin 50 na mutanen da ya nada ba, kuma ni ma ban san su ba, duk da kasancewar matar sa ta shekara 27,” inji ta.

 

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp