fidelitybank

Jita-Jita: Babu batun komawa jam’iyyar PRP daga APC – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta musanta jita-jitar da ke yawo cewar gwamnan jihar, Dr Abdullahi Umar Ganduje da tawagarsa na shirin sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa PRP.

Jita-jitar ta biyo bayan ganawar da ɓangaren APC na gwamnan ke yi a ƙoƙarin ɗaukaka ƙara kan hukuncin da wata kotu ta yi a Abuja game da zaben shugabanin jam’iyyar a mazabu da kananan hukumomin Kano.

Hukuncin kotun na ranar Juma’a ya baiwa ɓangaren Shekarau da ke rikici da ɓangaren gwamna Ganduje nasara.

Sai dai mai shari’a Hamza Muazu wanda ya zartar da hukuncin ya kuma buƙaci ɓangaren gwamna Ganduje da ke neman a yi watsi da shugabancin ɓangaren Shekarau ya biya tarar miliyan ɗaya.

An danganta shirin gwamnan na sauya sheka daga jam’iyyar ta APC, sakamakon hukuncin wanda ya ƙara zafafa rikicin APC a Kano tsakanin ɓangaren gwamnan da na tsohon gwamna Sanata Shekarau.

Sai dai cikin wata zantawa da BBC Hausa da kwamishinan raya karkara na jihar, Musa Iliyasu Kwankwaso, wanda ya na ɗaya daga cikin jiga-jigan ɓangaren na Ganduje, ya ce, batun ba shi da wani tushe ballantana makama.

Ya kara da cewa ,”Jam’iyyar APC ta mu ce, kuma za a ci gaba da kokarin yin sulhu, domin rikicin siyasa ba sabon abu ba ne kuma za a zo a daidaita idan har wadanda ke rikicin da su na nan cikin jam’iyyar ba su fita ba”

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp