Gwamnatin jihar Kano ta musanta jita-jitar da ke yawo cewar gwamnan jihar, Dr Abdullahi Umar Ganduje da tawagarsa na shirin sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa PRP.
Jita-jitar ta biyo bayan ganawar da ɓangaren APC na gwamnan ke yi a ƙoƙarin ɗaukaka ƙara kan hukuncin da wata kotu ta yi a Abuja game da zaben shugabanin jam’iyyar a mazabu da kananan hukumomin Kano.
Hukuncin kotun na ranar Juma’a ya baiwa ɓangaren Shekarau da ke rikici da ɓangaren gwamna Ganduje nasara.
Sai dai mai shari’a Hamza Muazu wanda ya zartar da hukuncin ya kuma buƙaci ɓangaren gwamna Ganduje da ke neman a yi watsi da shugabancin ɓangaren Shekarau ya biya tarar miliyan ɗaya.
An danganta shirin gwamnan na sauya sheka daga jam’iyyar ta APC, sakamakon hukuncin wanda ya ƙara zafafa rikicin APC a Kano tsakanin ɓangaren gwamnan da na tsohon gwamna Sanata Shekarau.
Sai dai cikin wata zantawa da BBC Hausa da kwamishinan raya karkara na jihar, Musa Iliyasu Kwankwaso, wanda ya na ɗaya daga cikin jiga-jigan ɓangaren na Ganduje, ya ce, batun ba shi da wani tushe ballantana makama.
Ya kara da cewa ,”Jam’iyyar APC ta mu ce, kuma za a ci gaba da kokarin yin sulhu, domin rikicin siyasa ba sabon abu ba ne kuma za a zo a daidaita idan har wadanda ke rikicin da su na nan cikin jam’iyyar ba su fita ba”