fidelitybank

Jirgin Kasa yayi awon gaba da Tirela da babur din Adaidaita Sahu a Kano

Date:

A na fargabar wasu fasinjojin sun mutu, yayin da wani jirgin kasa da ke tafiya ya murkushe motar tirela ta Siminti ta Dangote da wani Babur din Adaidai ta Sahu mai kafa uku a jihar Kano.

Lamarin ya faru ne a kan titin Obasanjo a cikin birnin Kano da misalin karfe 11:30 na safiyar Lahadi.

Shedun gani da ido da ke gudanar da sana’o’i a kusa da titin jirgin, sun ce, sun ga tirelar ta nufo layin dogo ne a lokacin da jirgin ke gudu.

Shaidu sun ce, sun yi yunkurin taimakawa tirelar, amma direban bai lura ba.

Jirgin kasan a lokacin da ya tsaya

“Lokacin da direban tirelar ya yi Æ™oÆ™arin ketare layin dogo, jirgin ya buge motar da babur É—in a lokaci guda,” in ji É—aya daga cikin shaidun.

Shaidu sun ce, tuni aka garzaya da fasinjojin da ke cikin babur din zuwa asibiti a sume, yayin da direban tirelar ya tsira da ransa.

Har ya zuwa lokacin da muke kawo wannan rahoton, tirelar har yanzu ta na kife a wajen wanda mutane suka zagaye  wajen, domin ganin bata gari basu kwashe buhunan siminti na cikin motar ba, yayin da jami’an tsaro suka baiwa motar kulawa, domin kar ‘yan ganima su kwashe kayan.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuÉ—in gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuÉ—in gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...
X whatsapp