‘Yan sanda a jihar Imo, sun harbe wani da ake zargin dan kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) da kuma Eastern Security Network (ESN) ne, a wani artabu da suka yi a dajin Onicha da ke karamar hukumar Ezinihitte Mbaise a jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, CSP. Michael Abattam, ya fitar ya ce, ‘yan bindigar da suka ga jami’an ‘yan sandan ne suka bude musu wuta. An kashe daya daga cikin ‘yan bindigar yayin da wasu suka kutsa cikin daji da ke kusa da wurin da harbin bindiga.
Sanarwar ta bayyana cewa; “Kungiyar ta’addanci ta IPOB/ ESN da ta haramtawa kungiyar ta’addanci, reshen ‘yan ta’addan ta sun yi dajin Onicha a karamar hukumar Ezinihitte Mbaise ta Jihar Imo inda suke fitowa suna aikata munanan laifuka da suka hada da ta’addanci, garkuwa da mutane, fashi da makami da kuma kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba”. In ji CSP Michael.
Sun kuma ce sun gano wani sansanin ‘yan ta’addar IPOB/ESN tare da gano wasu bama-bamai da makamai da alburusai a jihar.