fidelitybank

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Date:

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya ta tabbatar da kisan riƙaƙƙen ɗan bindigar da ya addabi wasu yankunan jihar.

Mai bai wa gwamnan jihar shawara kan harkokin tsaro, Ahmad Manga ya bayyana kisan Danbokolo a matsayin gagarumin nasara a yaƙi da matsalar tsaro.

”Danbokolo mutum ne da ya fi Bello Turji fitina, ya fi Turji aikata miyagun laifuka, illa kawai shi Turji sunansa da ya karaɗe kafofin yaɗa labarai”, in ji Ahmad Manga.

”Mutanensa da aka kashe sun haufa 100, saboda haka wannan gagarumar nasara ce a gare mu”, in ji jami’in gwamnatin Zamfarar.

Kacalla Danbokolo ya rasa ransa a wata arangama a ƙauyen Kurya, tsakanin jami’an sa kai na gwamnatin jihar Zamfara da mayaƙan ɗanbindigar.

Ana kallon mutuwar Danbokolo – wanda ake ganin a matsayin ubangidan Bello Turji – a matsayin cigaba a ɓangaren yaƙi da ƴanbindiga.

Donbokolo ya shafe shekaru masu yawa yana kai hare-hare yankunan jihar Zamfara tare da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Riƙaƙƙen ɗanbindigar ya gamu da ajalinsa ne tare da wasu ɗimbin mayaƙansa a lokacin da jami’an tsaron sa kai – da gwamnatin jihar Zamfara ta samar.

Mazauna yankin na kallonsa a matsayin mutum marar imani da tausayi da ya addabi yankunansu, ta hanyar kai hare-hare da kisan mutane.

“Shi mutum ne da bai yarda da sulhu ko ta wane hali ba, hatta ɗan’uwansa Bello Turji ya taɓa nuna alamun amincewa da sulhu, amma shi wannan bai taɓa nuna hakan ba”, kamar yadad wani mazaunin yankin ya bayyana.

Wannan ne karo na biyu da jami’an tsaro ke kashe riƙaƙƙun ƴanbindiga da ake ganin a matsayin iyayen gida da Bello Turji.

A watan Satumban 2024 ne jami’an sojojin ƙasar suka kashe Halilu Sububu, wanda ya shi ubangida ne ga Bello Turji a wani kwantan ɓauna da suka yi masa tare da mayaƙansa.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp