fidelitybank

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Date:

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya ta tabbatar da kisan riƙaƙƙen ɗan bindigar da ya addabi wasu yankunan jihar.

Mai bai wa gwamnan jihar shawara kan harkokin tsaro, Ahmad Manga ya bayyana kisan Danbokolo a matsayin gagarumin nasara a yaƙi da matsalar tsaro.

”Danbokolo mutum ne da ya fi Bello Turji fitina, ya fi Turji aikata miyagun laifuka, illa kawai shi Turji sunansa da ya karaɗe kafofin yaɗa labarai”, in ji Ahmad Manga.

”Mutanensa da aka kashe sun haufa 100, saboda haka wannan gagarumar nasara ce a gare mu”, in ji jami’in gwamnatin Zamfarar.

Kacalla Danbokolo ya rasa ransa a wata arangama a ƙauyen Kurya, tsakanin jami’an sa kai na gwamnatin jihar Zamfara da mayaƙan ɗanbindigar.

Ana kallon mutuwar Danbokolo – wanda ake ganin a matsayin ubangidan Bello Turji – a matsayin cigaba a ɓangaren yaƙi da ƴanbindiga.

Donbokolo ya shafe shekaru masu yawa yana kai hare-hare yankunan jihar Zamfara tare da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Riƙaƙƙen ɗanbindigar ya gamu da ajalinsa ne tare da wasu ɗimbin mayaƙansa a lokacin da jami’an tsaron sa kai – da gwamnatin jihar Zamfara ta samar.

Mazauna yankin na kallonsa a matsayin mutum marar imani da tausayi da ya addabi yankunansu, ta hanyar kai hare-hare da kisan mutane.

“Shi mutum ne da bai yarda da sulhu ko ta wane hali ba, hatta ɗan’uwansa Bello Turji ya taɓa nuna alamun amincewa da sulhu, amma shi wannan bai taɓa nuna hakan ba”, kamar yadad wani mazaunin yankin ya bayyana.

Wannan ne karo na biyu da jami’an tsaro ke kashe riƙaƙƙun ƴanbindiga da ake ganin a matsayin iyayen gida da Bello Turji.

A watan Satumban 2024 ne jami’an sojojin ƙasar suka kashe Halilu Sububu, wanda ya shi ubangida ne ga Bello Turji a wani kwantan ɓauna da suka yi masa tare da mayaƙansa.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp