Hukumar kula da jami’o’I ta kasa (NUC) ta kawo karshen fadan da a ken a mallakar wata jami’a dake garin Ogboko a jihar Imo, tsakanin Sanata Rochas Okorocha da gwamnatin jihar Imo.
Hakan ya biyo bayan gabatar da lasisin gudanar da jami’ar Kingsley Ozumba Mbadiwe da ke Ogboko a ranar Laraba ga gwamnatin jihar Imo da hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC) ta yi a Abuja.
Babban sakataren hukumar ta (NUC), Farfesa Abubakar Adamu ne ya gabatar da mika takardar shaidar jami’ar a wani taron da aka gudanar a shelkwatar hukumar.
PlatinumPost ta rawaito cewa, gwamnatin Hope Uzodinma ta dage cewa an gina jami’ar, wadda a baya ake kira Eastern Palm University, Ogboko, da dukiyar gwamnati, inda ta canza mata suna zuwa Jami’ar Kingsley Ozumba Mbadiwa, Ogboko, Jihar Imo.