fidelitybank

Jagoran kungiyar IPOB zai sake gurfana a gaban kotu

Date:

A yau ne ake sa ran sake gurfanar da jagoran ƴan awaren Biafra, Nnamdi Kanu da sabbin tuhume-tuhume 15 na ta’addanci a gaban kotu.

Sabbin tuhume-tuhumen wadanda aka gabatar da su ranar Litinin sun zo ne ƙasa da sa’o’i 24 kafin a sake shiga kotu a ci gaba da shari’ar da ake yi masa.

Nnamdi Kanu zai sake gurfana a kotun Abuja, bisa tuhumar cin amanar ƙasa da ta’addanci, da kafa haramtacciyar ƙungiya, laifukan da hukuncinsu hukuncin kisa ne idan sun tabbata.

Wannan ne karo na biyu da gwamnati ke yin kwaskwarima kan tuhume-tuhumen da ake yi wa jagoran na ƙungiyar IPOB.

An fara kama Kanu ne a 2015, bisa tuhume-tuhimen ta’addanci da jagorantar haramtaciyyar ƙungiya da wallafa munanan kalamai, da mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma shigar da miyagun kaya ƙasar ta Najeriya.

Nnamdi Kanu wanda ya ke da fasfo na ƙasar Birtaniya, kuma ya daɗe a ƙasar, sannan an mai da shi Najeriya, to amma har yanzu gwamnati ba ta bayyana daga wata ƙasa aka tissa ƙeyarsa ba.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp