fidelitybank

Jagoran kungiyar IPOB zai sake gurfana a gaban kotu

Date:

A yau ne ake sa ran sake gurfanar da jagoran ƴan awaren Biafra, Nnamdi Kanu da sabbin tuhume-tuhume 15 na ta’addanci a gaban kotu.

Sabbin tuhume-tuhumen wadanda aka gabatar da su ranar Litinin sun zo ne ƙasa da sa’o’i 24 kafin a sake shiga kotu a ci gaba da shari’ar da ake yi masa.

Nnamdi Kanu zai sake gurfana a kotun Abuja, bisa tuhumar cin amanar ƙasa da ta’addanci, da kafa haramtacciyar ƙungiya, laifukan da hukuncinsu hukuncin kisa ne idan sun tabbata.

Wannan ne karo na biyu da gwamnati ke yin kwaskwarima kan tuhume-tuhumen da ake yi wa jagoran na ƙungiyar IPOB.

An fara kama Kanu ne a 2015, bisa tuhume-tuhimen ta’addanci da jagorantar haramtaciyyar ƙungiya da wallafa munanan kalamai, da mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma shigar da miyagun kaya ƙasar ta Najeriya.

Nnamdi Kanu wanda ya ke da fasfo na ƙasar Birtaniya, kuma ya daɗe a ƙasar, sannan an mai da shi Najeriya, to amma har yanzu gwamnati ba ta bayyana daga wata ƙasa aka tissa ƙeyarsa ba.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...
X whatsapp