fidelitybank

Iya jam’iyya ta kadai zan marawa baya – Buhari

Date:

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa mambobin Jam’iyyarsa ta APC kaɗai zai mara wa baya a babban zaɓen ƙasar na 2023.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Mallam Garba Shehu ya fitar, Shugaba Buhari ya ce ba zai goyi bayan tsofaffin ƴan APC ko ma ƴan siyasar da suka gurfanar da APC a gaban kotu ba.

Sanarwar da aka fitar ranar Laraba ta ce “Buhari ya kasance soja mai ladabtarwa na APC kuma a zaɓen da ke tafe, zai mara baya ne kawai ga ƴan takarar Jam’iyyar.”

“Wannan gargaɗi ne ga ƴan jam’iyyar da suka sauya sheƙa da wadanda suka kai sahihan ƴan takarar APC kotu, su sani cewa ba ma tare da su kuma kar wani daga wajen Jam’iyyar da ya alaƙanta kansa da Shugaba Buhari.

“Shugaba Buhari yana son a ambato shi yana cewa shi ne yake riƙe da kujerar shugaban ƙasa da yardar Allah wanda ya yi amfani da Jam’iyyar APC wajen ba shi karagar mulki da kyakykyawan sakamako a 2015.”

A cewarsa, a 2019 ma ya lashe mafi yawan ƙuri’un da aka kaɗa kuma a karon farko da wani wanda ba ɗan PDP ba ya ɗare kan mulki bayan shekara 16 tana mulki.

Abin da Shugaban ƙasar ke cewa a kullum shi ne “ba zan yi yaudara ba ko kuma cin dunduniyar jam’iyyata ta hanyar marawa wasu ƴan takarar da ba na APC ba baya,” in ji sanarwar.

A sanarwar, Shugaba Buhari ya jaddada cewa furucinsa ko ɗaya ba wai yana sukar wani ɗan takara ba ne, sai dai ya ce maganar da ya yi ta nuna ƙarara cewa ƴan takarar da APC ta tsayar ne kawai za su samu goyon bayansa kuma sune waɗanda zai yi wa yaƙin zaɓe.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...
X whatsapp