fidelitybank

ISWAP ta tarwatsa ofishin ‘yan sanda a Borno

Date:

‘Yan ta’addar Daesh a lardin Yammacin Afirka, ISWAP, sun kashe dan sanda guda tare da dauke mota daya a wani hari da suka kai ofishin ‘yan sanda na Gubio a jihar Borno.

Wani kwararre a fagen yaki da masu tada kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a tafkin Chadi, Zagazola Makama, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a wani sako da ya wallafa a shafin X.

A cewar Zagazola, ‘yan bindigar sun zo ne a kan wasu motoci kirar Hilux guda biyu da kuma babura da dama kafin su yi ta harbe-harbe, inda suka far wa ofishin ‘yan sanda.

Ya rubuta cewa majiyoyi sun tabbatar da cewa wani Sufeto na ‘yan sanda ya biya mafi girman farashi yayin da yake hulda da ‘yan ta’addan.

An kuma bayyana cewa, ‘yan ta’addan sun yi awon gaba da wata mota kirar ‘yan sanda guda daya.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp