fidelitybank

INEC ta ki amincewa da takarar Akpabio

Date:

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ki amincewa da zaben fidda gwanin da ya samar da Sanata Godswill Akpabio, a matsayin dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a gundumar Akwa Ibom ta arewa maso yamma.

Akpabio, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, a daren ranar Talatar da ta gabata, a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar, ya janye takararsa na tsayawa takarar shugaban kasa na amincewa da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

A ranar 27 ga Mayu, 2022, Ekpoudom ya lashe zaben fidda gwani na Sanatan Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma domin samun tikitin APC.

Sai dai shugaban jam’iyyar na jihar, Stephen Ntuekpo, yayin da yake bayyana rashin tsaro a zaben fidda gwani na ranar 27 ga watan Mayu a gundumar, ya yi ikirarin cewa hedkwatar jam’iyyar APC ta kasa ta umurce shi da ya gudanar da wani sabon zaben fidda gwani a ranar 8 ga watan Yunin 2022.

Zaben fidda gwanin da aka yi ya haifar da Sanata Akpabio a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani. Ya samu kuri’u 478 daga cikin wakilai 512 da aka amince da su.

Sai dai kwamishinan zabe na jihar Akwa Ibom Mike Igini ya ce hukumar za ta amince da wanda ya lashe zaben fidda gwani da INEC ta sanyawa ido. A cewra The Will.

Igini, wanda ya zanta da Aminiya a ranar Lahadi a Uyo, babban birnin Jihar Akwa Ibom, ya musanta ikirarin cewa hukumar ta sa ido a kan zaben fidda gwani na ‘yan majalisar dattawa na APC, inda Akpabio ya yi nasara.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp