Kungiyar kare muradun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo, ya ce yawancin ‘yan kabilar Inyamurai ba su yarda da akidar ballewa daga Najeriya ba.
Shugaban kungiyar Ambassada, George Obiozor, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba.
Ya ce, “Idan Najeriya ta samu shugaban kasa dan kabilar Igbo, kasar da ‘yan kasar za su ga ainahin ma’anar tarayya ta hanyar adalci da daidaito”.
A sanarwar mai taken ‘’Igbo sun shirya neman shugabancin Najeriya a 2023’’, Obiozor ya ce, al’ummar yankinsu za su fi ‘yan Arewaci da ‘yan Kudu-maso-Yamma dunkulewa daya, idan suka samu shugabancin kasar.
Ya ce ya kamata a yi hankali da wadanda suke son yin amfani da wata dabara tasu ta siyasa, da suke daukar kudu maso gabashi a matsayin abokan gaba, wanda ba haka abin yake ba a cewarsa.
Ya kara da cewa galibin ‘yan kabilar Igbo ba su yarda da ballewa daga Najeriya ba.